Friday 19 October 2018

Ana tuhumar limaman coci da lalata yara a church



Ma'aikatar shari'a a Amurka ta bude bincike akan zargin cin zarafin yara ta hanyar lalata da ake yi wa daruruwan limaman cocin Roman Katolika.

Babban lauyan gwamnatin Jihar Pennsylvania ya aikewa akalla limamai 4 takardar neman su bayyana a kotu.
Masu gabatar da kara sun bukaci wasu takardun sirri da shaidu daga jami'an kotun.

A bangarenta cocin ta fitar da wata sanarwa inda ta tabbatar da cewa an aika musu da takardar neman bayyana a gaban kotu.

Sanarwar ta ce za ta bayar da cikakken hadin kai kan bukatar, kamar yadda ta bayar da hadin kai.

A watan Agusta wani rahotan tawagar lauyoyi ya gano sahihan shaidu da ke nuna cewa sama da yara dubu daya ne limaman coci 300 suka ci zarafinsu a fadin jihar ta Pennsylvania kuma jami'an kotu na rufa-rufa a kai.

SHARE THIS

Author:

Shafin Arewarmu.com shafine Dake Kawo Muku Fittatun Bayanai Akan Labaran Duniya, Labaran Gida, Hanyoyin Kiwon Lafiya, Fatawar Addinin Musulunci, Labarai Daga Kannywood, Labaran Garkuwar Jiki, Wakokin Hausa, Tafsiran Addinin Musulunci...

0 comments: