Monday, 7 August 2017

TIRKASHI: An Fara Zanga Zanga Neman Shugaban Kasa Buhari Yayi Murabus (Hotuna)

Wasu kungiyoyin al'umma sun yi zanga-zanga suna kira ga shugaban kasar Najeriya Muhammadu Buhari ko dai ya koma aiki ko kuma ya sauka.
A ranar Litinin ne wasu kungiyoyin al'umma suka yi zanga-zanga suna kira ga shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ko dai ya koma aiki ko kuma ya sauka.
Masu zanga-zangar sun ce sun shirya ta ne ganin cewa shugaba Buhari ya shafe kwanaki 92 yana jinya a birnin London, kuma har yanzu babu wani bayani kan yanayin rashin lafiyarsa ko kuma lokacin da zai koma bakin aiki.
Wani mawaki mai suna Charly Boy ne ya shirya zanga-zangar wacce ba ta samu halartar mutane da dama ba.
Mutanen sun yi ta daga kyallaye da ke dauke da rubuce-rubuce da dama na neman shugaban ya sauka daga mulki.
Gomman masu zanga-zangar sun faro ne daga dandalin Unity Fountain da ke birnin tarayya Abuja, inda suka dire a kwanar shiga fadar shugaban kasa, bayan da jami'an tsaro suka dakatar da su.
Daga cikin kungiyoyin da suka halarci zanga-zangar har da kungiyar 'yan uwa Musulmai ta Shi'a da ke kira da a saki shugabanta Malam Ibrahim El-Zakzaky
MAsu zanga-zangar dai sun ce za su ci gaba da yin zaman dirshan a wajen har sai sun ga abin da ya turewa buzu nadi.

SHARE THIS

Author:

Shafin Arewarmu.com shafine Dake Kawo Muku Fittatun Bayanai Akan Labaran Duniya, Labaran Gida, Hanyoyin Kiwon Lafiya, Fatawar Addinin Musulunci, Labarai Daga Kannywood, Labaran Garkuwar Jiki, Wakokin Hausa, Tafsiran Addinin Musulunci...

0 comments: