Tuesday, 10 July 2018

Makwabcin Sheikh Kabiru Gombe ya kai kararsa gaban kotu kan zarginsa da aikata wani lafi

Fitaccen malamin addinin Musuluncin nan ya amsa sammacin da wata kotun jihar Kano ta aike masa sakamakon kararsa da wani makwabcinsa ya shigar akansa, kamar yadda jaridar Alfijir ta ruwaito.
Shi dai wannan makwabci na Malam Kabiru Gombe yayi kararsa ne gaban kotu kan zarginsa da take akan  hakkin makwabtaka, kamar yadda ya shaida ma alkalin kotun, Sarki Yola.

makwabcin yana fadin wai Kabiru Gombe ya sanya wasu waga wagan Tagogi a sabon gidansa daya gina a unguwar Sabuwar Gandu, inda makwabcin ke zarginsa da samun damar liken matayensu.


Makwabcin ya kara da cewa “Wannan Malamin ya gina manyan tagogi, sa’annan ya sanya musu bakaken gilasai, ta yadda shi zai iya ganin jama’a, amma mu ba zamu gan shi ba.”
Wannan makwabci dai ya cigaba da shaida ma kotu cewar tun lokacin da aka fara ginin gidan suka janyo hankalin Malamin, amma bai dauki wani mataki game da hakan ba.
Sai dai lauyan Malamin Ishaq Adam Ishaq ya bayyana ma kotu cewar ba wani bane ke damun wannan makwabci illa bakin ciki da hassada da suke yi da Malamin sakamakon daukaka da Allah yayi masa.

Daga karshe dai Alkali Sarki Yola ya aika da jami’an kotu da su tafi su gano masa yadda wadannan tagogi suke, sa’annan su kawo masa rahoton abinda suka gani, bayan nan sai a cigaba da sauraron karar.


SHARE THIS

Author:

Shafin Arewarmu.com shafine Dake Kawo Muku Fittatun Bayanai Akan Labaran Duniya, Labaran Gida, Hanyoyin Kiwon Lafiya, Fatawar Addinin Musulunci, Labarai Daga Kannywood, Labaran Garkuwar Jiki, Wakokin Hausa, Tafsiran Addinin Musulunci...

0 comments: