Monday, 9 July 2018

Shawarata ga mata wadanda ke son shigowa fim- Fatima Abubakar Shu'uma

Shararriyar jarumar nan ta wasan fina-finan Hausa a masana'antar Kannywood ta baiwa dukkan masu sha'awar shiga a dama da su a harkar fina-finai musamman ma mata da su tabbata sun samu amincewar iyayen su tukuna.

Jarumar dai ta bayyana hakan ne a lokacin da ake fira da ita a gidan talabijin din nan na Hausa na Arewa24 a cikin shirin Ga Fili Ga Mai Doki na Kundin Kannywood tare da mashiryin shirin  Aminu Shariff.
jarumar ta kuma shawarci matan da su zama masu hakuri musamman ma da masoyan su da a kullum za su yi ta yin tururuwa domin kawowa gare su.

Haka ma dai jarumar ta bayyana cewa jaruma Jamila Nagudu ce tafi burge ta a cikin jaumai mata sannan kuma Adam A. Zango ne yafi burge ta a cikin jarumai maza a masana'antar.



SHARE THIS

Author:

Shafin Arewarmu.com shafine Dake Kawo Muku Fittatun Bayanai Akan Labaran Duniya, Labaran Gida, Hanyoyin Kiwon Lafiya, Fatawar Addinin Musulunci, Labarai Daga Kannywood, Labaran Garkuwar Jiki, Wakokin Hausa, Tafsiran Addinin Musulunci...

0 comments: