Wasu 'yan Najeriya sun soma yin caca a kan ranar da shugaban kasar Muhammadu Buhari, wanda ya shafe kusan wata uku yana jinya a birnin London, zai koma kasar.
Wani shafin intanet da ke yin caca, NaijaBet.com, na tambayar mutanen da ke da sha'awar cacar su canki ranar da shugaban kasar, wanda ya fice daga Najeriya ranar bakwai ga watan Mayu, zai koma gida.
A watan Yunin shekarar 2016 ne shugaban, mai shekara 74 a duniya, ya soma tafiya London domin yin jinyar abin da, a wancan lokacin, jami'an gwamnati suka bayyana da ciwon kunne.
A farkon wannan shekarar ma Shugaba Buhari ya koma London inda aka duba lafiyarsa.
A lokacin da ya koma kasar a watan Maris, ya ce an yi masa karin jini, ko da yake bai fadi larurar da yake fama da ita ba.
Sai dai shugaban na Najeriya ya ce bai taba yin jinya irinta ba a rayuwarsa.
A watan jiya ne mukaddashin shugaban kasar Yemi Osinabjo ya ziyarci Shugaba Buhari a London, kuma ya ce shugaban yana samun sauki.
Thursday, 3 August 2017
Author: Arewarmu Concepts
Shafin Arewarmu.com shafine Dake Kawo Muku Fittatun Bayanai Akan Labaran Duniya, Labaran Gida, Hanyoyin Kiwon Lafiya, Fatawar Addinin Musulunci, Labarai Daga Kannywood, Labaran Garkuwar Jiki, Wakokin Hausa, Tafsiran Addinin Musulunci...
RELATED STORIES
Kwace akwatin zabe: Sojoji sun sha alwashin bin umarnin Buhari su bindige mutumKwace akwatin zabe: Sojoji sun sha alwashin bin u
A wani Al'amari me kamada Tilastawa: ansa wata Budurwa 'Yar shekara 15 ta Auri wani dattijo me shekara 75.A wani Al'amari me kamada Tilastawa: ansa wata Bu
An kashe mutane 66 a wasu unguwani a jihar Kaduna A kalla mutane 66 ne aka kashe a wasu ungu
Hotunan yadda aka rantsar da Shugaba Buhari a dandalin Eagle Square da ke Abuja. Hotunan yadda aka rantsar da Shugaba Buhari a da
Yayinda ake kai ruwa rana kan mafi karancin kudi N30,000 a Najeriya, kasar Afrika ta kudu ta kara nata zuwa N126,480 Kasar Afrika ta kudu ta kara kudin albashin
An Kai Mummunan Farmaki A Ofishin Kamfen Din Atiku Da Ke Katsina Jaridar Katsinapost ta fitar da rahoton cewa
0 comments: