Wednesday, 15 March 2017

Dalilan da Suka Hana Ibrahim Magu Dacewa da Amincewar Majalisa

Duk da cewa wannan shine karo na biyu da shugaban hukumar EFCC, Ibrahim Magu yake bayyana a majalisar dattijai a wannan karon ma bata haifar da da mai Ido ba.

Magu ya bayyana yau kuma ya amsa duka tambayoyin da ‘yan majalisar suka tambayeshi amma kash, majalisar bata amince da bayanan da ya bada kan rahoton hukumar tsaro na sirri wato SSS in da tace Magu ba mutumin kirki bane da za’a amince da shi.

Cikin dalilan da ya sa majalisar taki amincewa da tabbatar da shi shugaban hukumar EFCC din shine wai an taba kama Magu ta takardun hukumar EFCC a gidansa a wancan lokacin wanda hakan saba ma doka ce.

Da akayi masa wannan tambaya, Magu ya tabbatar da hakan amma yace ko a wancan lokacin da aka tambayeshi bayanai akan tafiya da takardun gida da yayi yace ya kai su gida ne domin ya ci gaba da aiki.

Bayan haka an tuhumeshi da zama a gidan wani jami’in soji da ake tuhuma da laifin cin hanci da rashawa, anan ma Magu ya ce bai taba zama a gidan wannan mutumi ba.

Ya shaida wa majalisar cewa gidan da yake zama aciki gidan gwamnati ne wanda gwamnati ta ke biya masa.

Na uku kuma cikin dalilan shine rashin goyon bayan da bai samu ba daga wajen sanatoci.

Yanzu dai haka ya rage wa mai shiga rijiya, ko shugaban kasa Muhammadu Buhari ya mika sunan wani, ko kuma ya bar Ibrahim Magu ya ci gaba da zama a kujeran shugaban cin hukumar na wucin gida har sai an nada wani.

SHARE THIS

Author:

Shafin Arewarmu.com shafine Dake Kawo Muku Fittatun Bayanai Akan Labaran Duniya, Labaran Gida, Hanyoyin Kiwon Lafiya, Fatawar Addinin Musulunci, Labarai Daga Kannywood, Labaran Garkuwar Jiki, Wakokin Hausa, Tafsiran Addinin Musulunci...

0 comments: