Tuesday, 7 March 2017

Gwamnatin Jihar Kaduna Ta Hana Acaba Da Bara Akan Tituna

Gwamnatin jihar Kaduna ta sanar da hana Acaba da bara a tituna da manyan biranen jihar.
Gwamnati ta ce daga yau za’a kama duk wanda ya ke yin Acaba ko kuma aikata bara a manyan tinunan jihar.

Kakakin gwamnan jihar Kaduna Samuel Aruwan ne ya fitar da sanarwan bayan taron kwamitin tsaron tsaron jihar da akayi a fadar gwamnatin jihar.

Sanarwan ta ce da ma can akwai dokar hana Acaba a jihar an dan daga kafa bne domin gwamnati ta gama wasu ayyuka da takeyi, amma daga yau an dakatar da hakan.


SHARE THIS

Author:

Shafin Arewarmu.com shafine Dake Kawo Muku Fittatun Bayanai Akan Labaran Duniya, Labaran Gida, Hanyoyin Kiwon Lafiya, Fatawar Addinin Musulunci, Labarai Daga Kannywood, Labaran Garkuwar Jiki, Wakokin Hausa, Tafsiran Addinin Musulunci...

0 comments: