Wasu ma’aurata, Nasiru Adeyemo da matarsa Idayat Adeyemo sun shiga komar jami’an Yansanda bayan da aka kama sud da zargin kokarin salwantar da rayuwar yarsu mai shekaru 7, Abibat Anike Adeyemo.
Yansanda sun Ankara da halin daa wannan yarinya ta shiga ne bayan da jama’a suka gulmata musu bayyanar wani farin buhu akan hanya, wanda yake a daure, inda ba tare da wata wata ba, Yansanda suka dira wajen.
Kaakain rundunar Yansandan jihar ASP Abimbolaa Oyeyemi yace samun labarin ya sanya DPO dake rike da yankin ya jagoranci tawagar yansanda zuwa wajen, idna suka tarar da buhun, kwance shi keda wuya suka tarar da yarinyar a ciki a sume, tare da yatsar ta na hannun dama a guntule.
Daga nan ne yansanda suka garzaya da yarinyar asibiti, inda aka ceto rayuwarta, bayan ta kwashe kwanaki 2 daure a cikin buhun, kamar yadda Arewarmu.com ta ruwaito.
Baya da farfado ne sai yarinyar ta shaida ma yansanda cewa mahaifinta da kishiyar babarta ne suka guntule mata yatsan hannunta, sa’annan suka daure ta a cikin buhun, suka jefar tun ranar juma’a data gabata.
Jin wannan labara ya sanya yansanda baza komarsu wajen neman iyayen wannan yarinya ruwa a jallo, inda suka samu nasarar kama su a ranar Lahadi 13 ga watan Agusta. Kuma tuni an fara bincike akansu.
Thursday, 17 August 2017
Author: Arewarmu Concepts
Shafin Arewarmu.com shafine Dake Kawo Muku Fittatun Bayanai Akan Labaran Duniya, Labaran Gida, Hanyoyin Kiwon Lafiya, Fatawar Addinin Musulunci, Labarai Daga Kannywood, Labaran Garkuwar Jiki, Wakokin Hausa, Tafsiran Addinin Musulunci...
RELATED STORIES
Yadda matar aure ta mutu a lokacin jima’i da saurayi a gidan saukar baki Matar wani mazaunin jihar Lagas ta mutu a gidan
An Yankewa Wani Dan Kasuwa Hukuncin Daurin Shekaru 140 A Gidan YariMai shari’a Mohammed Idris na babbar kotun tarayy
Wannan bala’i da me yayi kama? Uwa ta siyar da jaririyarta N50,000 don samun na kashewaWata Karuwa mai shekaru 22, Blessing Udoh ta gurf
Ladan noma: Wani manomi ya dauki alwashin saya ma Buhari takardar takaraWani manomi da cikin manoman da suka amfana da ts
Duniya Tazo Karshe: Ga Matarsa Amma Ya Zabi Yayiwa Yarsa FyadeWata ýar kasuwa dake zaune a Ibadan, Misis Aminat
KAI DUNIYA: Fasto Ya Yiwa Masoyiyarsa Yankan Rago (Hotuna)Rundunar yansandan jihar Ogun ta cafke wani Malam
0 comments: