A kalla mutum goma sha daya ne suka mutu, sannan wasu 17 suka jikkata a wani harin bam da aka kai bakin tashar motar Muna da ke birnin Maiduguri, a Arewa maso Gabashin kasar.
Ana zargin mayakan boko-haram da kai harin, inda 'yan kunar bakin-wake biyu suka mutu.
Mazauna birnin Maiduguri na jihar Borno a Najeriya sun ce sun ji karar fashewar wasu abubuwa uku da ake zargin bama-bamai ne a ranar Alhamis da daddare.
Bayani na nuna cewa wasu da ake zargin 'yan Boko Haram ne da suka yi yukurin shiga birnin suka tayar da abubuwan, sai dai sojoji sun dakile yunkurin.
Ko da yake kawo yanzu babu cikakken bayanin asarar rayukan da aka samu daga hukumomi, wasu na fargabar an samu jikkata kuma wasu sun mutu.
Rahotanni sun bayyana cewa 'yan Boko Haram din sun yi kokarin shiga Maiduguri ne ta Yerwa ta Custom House, sai dai ba su yi nasara ba.
Ganau da kuma sojoji sun ce mutane 11 ne suka ransu a yayin da mayakan Boko Haram din ke kokarin fatattakar 'yan kunar bakin wake a wajen birnin Maidugurin.
Ana zargin mayakan boko-haram da kai harin, inda 'yan kunar bakin-wake biyu suka mutu.
Mazauna birnin Maiduguri na jihar Borno a Najeriya sun ce sun ji karar fashewar wasu abubuwa uku da ake zargin bama-bamai ne a ranar Alhamis da daddare.
Bayani na nuna cewa wasu da ake zargin 'yan Boko Haram ne da suka yi yukurin shiga birnin suka tayar da abubuwan, sai dai sojoji sun dakile yunkurin.
Ko da yake kawo yanzu babu cikakken bayanin asarar rayukan da aka samu daga hukumomi, wasu na fargabar an samu jikkata kuma wasu sun mutu.
Rahotanni sun bayyana cewa 'yan Boko Haram din sun yi kokarin shiga Maiduguri ne ta Yerwa ta Custom House, sai dai ba su yi nasara ba.
Ganau da kuma sojoji sun ce mutane 11 ne suka ransu a yayin da mayakan Boko Haram din ke kokarin fatattakar 'yan kunar bakin wake a wajen birnin Maidugurin.
0 comments: